Haka kuma, sojojin Isra'ila sun ce, a wannan rana, sun gano Falesdinawa guda biyu a kan yankin dake tsakanin arewacin Gaza da Isra'ila, a kokarinsu na shiga cikin Isra'ila daga yankin Gaza. Sun kuma kara da cewa, a yayin da suke bin wadannan mutane biyu, wasu Palasdinawa suka rika harbinsu da bindigogi daga yankin Gaza, sa'an nan, sojojin Isra'ila sun mayar da martani ta hanyar harba boma-bomai zuwa wani wurin da Falesdinawa ke sintiri.
Jami'an tsaron yankin Gaza sun bayyana cewa, a wannan rana, sojojin Isra'ila sun harba boma-bomai zuwa wani wurin sintiti na kungiyar Hamas ta Falesdinu dake arewacin yankin Gaza. (Maryam)