Daga cikin wadanda suka samu raunuka, akwai mata 9, da kananan yara 4, kana 3 daga cikinsu sun samu raunuka masu tsanani, bayan da sojojin Isra'ila suka harbesu a kai, yayin da ragowar mutanen suka samu kananan raunuka.
Duk da irin yanayi zafi da ake fama da shi a lokacin azumin watan Ramadan, wata mai tsarki wanda al'ummar musulmi ke gudanar da ibadun azumi, Falastinawa na cigaba da yin zanga zanga a yankunan dake kan iyakar zirin Gaza.
Sama da Falastinawa 120 ne aka hallaka, kana an jikkata dubbai, a yayin da jami'an tsaron Isra'ila suka bude wuta kan dandazon Falasdinawa dake zanga zanga kan iyakar zirin Gaza a ranar 30 ga watan Maris.
Su dai al'ummar Falastinawa suna zanga zangar neman hakkokinsu ne na matsugunansu da yahudawa 'yan kama wuri zauna suka mamaye mai dadadden tarihi tun daga shekarar 1948. (Ahmad)