in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD ya kira taron gaggawa kan yanayin zirin Gaza
2018-05-19 16:24:59 cri
A ranar 18 ga wata, kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD ya kira taron gaggawa don yin tattaunawa kan yanayin da ake ciki a zirin Gaza, inda aka tsai da kudurin tura tawagar bincike zuwa yankin, domin gudanar da bincike kan yankin Falesdinu da aka mamaye, da kuma keta hakkin dan Adam dake faruwa a yankin Gaza.

A wannan rana kuma, shugaban ofishin siyasa na kungiyar Hamas Ismail Haniyeh, ya gabatar da jawabi a wani masallaci dake birnin Gaza cewa, ba za a tsayar da zanga-zangar ba, har sai Isra'ila ta dena mamayar da ta yiwa yankin Gaza. Kana, ya kuma yi kira da a fadada wuraren gudanar da zanga-zangar zuwa yankin yammacin kogin Jordan.

Koda yake, wannan rana ita ce ranar Jumma'a ta farko bayan da aka shiga watan Azumi, 'yan Falesdinu da dama sun fita yin zanga-zangar a yankin dake kan iyakar tsakanin Falesdinu da Isra'ila a zirin Gaza. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China