Rundunar Isra'ila ta ce, harin da aka kai a wannan karo mayar da martani ne kan harin da Hamas ta kaiwa sojojin Isra'ila da aka jibge a iyakar Gaza, sai dai kuma babu wani sojan Isra'ila da ya ji rauni sakamakon wannan hari.
Rahotanni na cewa, yanayi na kara tsanantawa tsakanin Palasdinu da Isra'ila. A ranar 14 ga wata ne dai Amurka ta sanar da bude ofishin jakadancinta dake Isra'ila a birnin Kudus, lamarin da ya haifar da barkewar zanga-zangar a birane da dama na Palasdinu a wannan rana, inda masu zanga-zanga suka yi arangama da sojin Isra'ila, abin da ya haddasa rasuwar Palasdinawa fiye da 60 yayin da wasu 3000 suka ji rauni. (Amina Xu)