in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila za ta hana Iran kara jibge makamai a kasar Sham
2018-05-07 16:04:49 cri

Firaministan Isra'ila Benjamin Netayahu, ya bayyana a jiya yayin taron ministocin kasar cewa, Isra'ila za ta hana Iran kara jibge makamai a Sham.

Ya ce, a cikin watannin da suka gabata, rundunar IRGC ta Iran ta jigbe wasu makamai na zamani a kasar Sham don kai hari kan Isra'ila, ciki hadda jirgin sama maras matuki da makamai masu linzami da dai sauransu. A cewarsa, Isra'ila ba ta son tsananta halin da ake ciki a yankin, amma ta yi shiri tsaf don mayar da martani, ya ce, Isra'ila za ta yi iyakacin kokarin hana matakin sojan da Iran za ta dauka kanta, duk da cewa za a tada wani yaki tsakaninsu.

Ban da wannan kuma, Netayahu ya shedawa manema labarai bayan taron cewa, yarjejeniyar nukiliyar Iran ba ta da kyau ko kadan, kuma ya kamata a gyara ta duka ko hana aiwatar da ita baki daya, idan ba haka ba, Iran za ta kafa wani sansanin makaman nukiliya cikin gajeren lokaci.(Amina Xu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China