in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nuna damuwa game da tashe-tashen hankula a yankin Gaza
2018-05-19 16:22:58 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin dake ofishin MDD a birnin Geneva, kana, a sauran kungiyoyin kasa da kasa dake kasar Switzerland Yu Jianhua, ya bayyana a ranar 18 ga wata cewa, kasar Sin ta nuna damuwa matuka dangane da barkewar rikice-rikice a zirin Gaza, wadanda suka haddasa rasuwar mutane da dama, inda ta yi kira ga Isra'ila da Falesdinu, musamman bangaren Isra'ila da su kai zuciya nesa, don kaucewa sake tabarbarewar yanayi a yankin.

A yayin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD game da halin da ake ciki a Gaza, Yu Jianhua ya bayyana cewa, kasar Sin ba ta goyi bayan yin amfani da makaman da ba su dace ba, kuma ta bukaci bangarorin da abin ya shafa da su dakatar da aikace-aikacensu na tada hankulan al'umma. Kana, ya ce, kasar Sin tana goyon bayan kudurin da kwamitin sulhu na MDD ya tsai da domin gaggauta dawowar Isra'ila da Falesdinu teburin yin shawarwarin neman sulhu, ta yadda za a warware batun birnin Kudus ta hanyar zaman lafiya da yin shawarwari.

Haka kuma, ya ce, kasar Sin ta fidda manufofi guda hudu domin warware matsalar Falesdinu, kuma tana son yin shawarwari da gamayyar kasa da kasa kan batun Falesdinu a koda yaushe, ta yadda za a warware matsalar bisa dukkan fannoni, kuma cikin yanayin adalci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China