in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban magatakardan MDD ya nuna damuwa kan karuwar rikice-rikice a Yemen
2018-05-10 13:37:00 cri
Babban magatakardan MDD Antonio Guterres, ya fidda sanarwa ta bakin kakakinsa a jiya Laraba, wadda ke nuna damuwarsa matuka game da karuwar rikice-rikice a kasar Yemen, inda ya bukaci sassan da ba sa ga maciji da juna da su kai zuciya nesa.

Haka kuma, ya jaddada cewa, ya kamata bangarorin da rikicin ya shafa su bi dokar jin kai ta kasa da kasa, domin za a yi bincike da kuma gurfanar da wadanda suka aikata laifuka gaban kuliya. Daga bisani kuma, Mr. Guterres ya ba da shawarar cewa, ya kamata sassa daban daban na kasar Yemen su yi shawarwari domin neman hanyar siyasa, wadda ita ce hanya kadai da za a iya bi wajen warware rikicin kasar, da kuma tabarbarewar yanayin jin kai.

A ranar 7 ga wata, jiragen saman yaki na wasu kasashe dake karkashin jagorancin kasar Saudiya, sun kai hari kan fadar shugaban kasar Yemen dake birnin Sana'a, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane a kalla guda 6. Sa'an nan kuma, a ranar 9 ga wata, dakarun kungiyar al-Ḥuthiyyun sun harba makamai masu linzami da dama zuwa kasar Saudiya, domin mai da martani gare ta. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China