in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Luguden wuta da dakarun kawancen da Saudiyya ke jagoranta ya yi sanadin rayuka fiye da 40 a kudu masu yammacin Yemen
2017-12-27 11:19:23 cri
Kafafen watsa labarai na kasar Yemen sun ruwaito cewa, Jiragen yakin dakarun kawancen da Saudiyya ke jagoranta, ya yi luguden wuta kan dandazon mutane a wata fitacciyar kasuwa dake lardin Taiz na kudu maso yammacin kasar, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 40.

Shaidun dake kusa da kasuwar sun fadawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, luguden wutan ya rutsa da mutane da dama, saboda ya faru ne lokacin da mutane suka fi hada-hada a kasuwar da ta cika da mutane da suka je sayayya daga makwabtan kauyuka.

A bangare guda kuma, ana ta kwabza fada tsakanin dakarun kasar dake samun goyon bayan dakarun kawance da Saudiyya ke jagoranta da kuma 'yan tawayen Houthi a larduna daban-daban na kasar.

Tun cikin watan Maris din 2015 ne dakarun kawancen suka shiga yakin kasar Yemen, domin fatattakar 'yan tawayen Houthi da mara baya ga Gwamnatin da kasashen duniya ke marawa baya ta Shugaba Abd-Rabbu Mansour Hadi, wanda 'yan tawayen suka tilastawa gudun hijira.

Kawo yanzu, yakin ya yi sanadin mutuwar 'yan kasar sama da 10,000, galibinsu yara, tare da raba wasu miliyan 3 da gidajensu, al'amarin da ya haifar da daya daga cikin matsalolin jin kai mafi muni a duniya. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China