in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Yemen da Saudiyya ke marawa baya, ya kaddamar da Garambawul kan Jami'an Gwamnatinsa
2017-12-25 10:35:46 cri
Shugaban kasar Yemen da Saudiyya ke marawa baya Abdu-Rabbu Mansour Hadi, ya kaddamar da tangade da rairaya kan jami'ansa, inda ya kori Ministan harkokin cikin gidan kasar da wasu ministoci 3.

Wata sanarwa da ofishin Shugaban kasar ya fitar jiya, ta ce an sauya jami'ai 4 cikin jami'an Firaministan kasar Ahmed Obeid bin Dagr, ciki har da maye gurbin Ministan harkokin cikin gida Hussein bin Arab da Ahmed bin Ahmed Maisari.

Masu sanya ido na ganin cewa, umarnin Shugaban kasar da ya kai ga korar Gwamnonin Lahj da al-Dhalea ka iya janyo kin amincewa da fusata daga mutanen yankin kudancin kasar, wanda ka iya kawo tashin hankali da rashin tsaro.

Gwamnatin Yemen mai samun goyon kasashen waje da hadin gwiwar dakarun kawance da Saudiyya ke jagoranta, sun shafe sama da shekaru biyu suna yaki da 'yan tawayen Houthi dake samun goyon bayan Iran game da jan ragamar da kasar.

Wata Kididdigar MDD ta nuna cewa, tun bayan da dakarun kawancen ta shiga cikin yakin basasar Yemen, sama da mutane 10,000 galibinsu fararen hula sun mutu, sannan wasu kusan miliyan 3 sun rasa matsugunansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China