Jiya Litinin a birnin Toronto na kasar Canada, ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar G7 sun bayyana cewa, kungiyar ta yi alkawarin kara kiyaye dokokin kasa da kasa, ciki had da harkokin ciniki, a kokarin daidaita manyan kalubalolin tattalin arziki da tsaro ta fuskar siyasa.
An gudanar da taron ministocin harkokin waje da na tsaro na kungiyar G7 ne daga ranar 22 zuwa 24 ga wata, wanda ya share fagen taron koli na kungiyar da za a gudanar a watan Yunin bana a birnin Quebec na kasar Canada. (Tasallah Yuan)