in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres ya jaddada muhimmancin G77 da kasar Sin wajen inganta ra'ayin kasancewar bangarori da dama
2017-09-23 13:48:22 cri
A yayin taron ministoci na shekara-shekara na kungiyar G77 da kasar Sin da aka shirya a jiya Juma'a, babban sakataren MDD Antonio Guterres ya tabbatar da muhimmiyar rawar da kungiyar G77 da kasar Sin ke takawa kan inganta ra'ayin kasancewar bangarori da dama da kuma neman dauwamammen ci gaba.

A yayin taron, Guterres ya jaddada cewa, kungiyar G77 da kasar Sin suna da muhimmanci sosai wajen cimma burin neman dauwamammen ci gaba, da karfafa ra'ayin kasancewar bangarori da dama. A cewarsa, kungiyar ta nuna karfin jagoranci na hadin kai, ta shugabancin hadin kai tsakanin kasashe masu tasowa, kana ta nuna amfanin dangantakar abokantaka ta hadin kai kan fannonin tattara albarkatu da nuna goyon baya.

Baya ga haka, Guterre ya bayyana fatansa na ganin za a ci gaba da karfafa dangantakar abokantaka ta hadin kai a tsakanin MDD da kungiyar G77 da kasar Sin ta fuskar inganta ajandar neman dauwamamman ci gaba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China