in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya shugabanci taron takwarorinsa na kasashe mambobin SCO
2018-04-24 20:31:35 cri

Yau Talata a nan Beijing, Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya shugabanci taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar hadin kan Shanghai wato SCO, inda ya gabatar da shawarwari 6 kan yaddaz za a zurfafa hadin gwiwa a tsakanin mambobin kungiyar a sabon yanayin da ake ciki.

Ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar da suka halarci taron sun yaba wa kokarin da kasar Sin take yi wajen kara inganta ayyukan kungiyar a matsayinta na shugaban kungiyar na wannan karo. Sun kuma nuna fatansu na taimakawa kasar Sin ta yadda za a samu sakamako mai kyau a yayin taron koli na Qingdao. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China