Wannan kudurin ya tabbatar da muhimmin aikin na MONUSCO, wato wajen kiyaye fararen hula, da kuma tabbatar da yarjejeniyar siyasa da bangarori daban daban na kasar Kongo Kinshasa suka cimma a ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2017 da dai sauransu.
Baya ga haka, kudurin ya taimakawa MONUSCO wajen fatattakar dakaru masu dauke da makamai na kasar, ta hanyar kai dauki daga dakarun soji, kana da sa ido, da bada rahoto kan yanayin take hakkin bil Adama da na saba dokar jin kai ta kasa da kasa. (Bilkisu)