in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta maida martani kan harin da wasu kasashe suka kaiwa Siriya
2018-04-14 18:16:36 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, kasar ba ta amince da duk wani yunkuri na daukar matakan soja tsakanin kasa da kasa ba, kana, duk wani matakin soja da aka dauka ba tare da samun izini daga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ba, ya sabawa dokokin Majalisar da na kasa da kasa, kuma zai kara haifar da matsala ga batun warware matsalar Siriya.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ce ta bayyana haka, yayin da take amsa tambayoyin 'yan jaridu dangane da luguden wuta kan kasar Siriya da Amurka da Birtaniya da kuma Faransa suka yi da sanyin safiyar yau Asabar

Madam Hua ta kuma jaddada cewa, kasar Sin tana ganin cewa, ya kamata a gudanar da bincike daga dukkan fannoni bisa hanya madaidaiciya, kan zargin da ake wa Siriya na amfani da makamai masu guba, ta yadda za'a samu sakamako mai tushe. Sin ta ce, ya kamata kasashe daban-daban su ci gaba da goyon-bayan MDD wajen shiga-tsakani kan rikicin Siriya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China