in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira da a yi hangen nesa game da batun Syria
2018-04-14 13:55:50 cri
Wakilin kasar Sin na din din din a MDD Ma Zhaoxu ya yi kira ga dukkan bangarori su kwantar da hankali tare da yin hangen nesa game da lamarin Syria.

Ma Zhaoxu ya shaidawa kwamitin sulhu na MDD cewa, yanayin da ake ciki a Syria na matukar hadari, wanda ya ce yana kan wata gaba mai muhimmaci na zabi tsakanin zaman lafiya da yaki.

Ya ce a wannan lokaci da al'amura suka tsananta, ya kamata kwamitin sulhun ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa, na gina hadin kai da cimma matsaya tare da yin abun da ya kamata domin hana barkewar yaki.

Ya ce a ko da yaushe, kasar Sin ta fi mayar da hankali kan hawa teburin sulhu wajen warware rikici, inda kuma ta kasance mai adawa da amfani da karfi ko yin barazanar amfani da karfi a harkokin kasa da kasa.

Jami'in na kasar Sin ya ce yin gaban kai wajen daukar matakan soji ta hanyar kaucewa kwamitin, ya saba da dokoki da manufofin kwamitin da kuma dokokin da ka'idojin kasa da kasa.

Ya ce ya kamata a girmama cikakken ikon da Syria ke da shi da ikon kasancewarta matsayin kasa daya dunkulalliya mai cin gashin kanta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China