in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya bayyana damuwa game da harin da aka kai Syria karkashin jagorancin Amurka
2018-04-14 17:29:23 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya bayyana damuwa game da hari ta sama da Amurka ta jagoranci kai wa Syria, yaan mai cewa, aikin kwamitin sulhu na Majalisar shi ne tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya.

Wata sanarwa da Sakatare Janar din ya fitar jiya ta ruwaito shi ya na cewa, ya na bibiyar rahotonnin hare- hare ta sama da Amurka da Birtaniya da Faransa suka kai Syria. Ya ce akwai wani nauyi, musammam yayin da ake batun zaman lafiya da tsaro, na yin biyayya ga dokokin MDD da ma na kasa da kasa.

Ya bukaci kasashe mambobin Majalisar su yi hangen nesa a wannan yanayi mai cike da hadari tare da kaucewa yin abubuwan da ka iya tsananta halin da ake ciki da kuma wahalhalun al'ummar Syria. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China