in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban magatakardan MDD ya bukaci kwamitin sulhun MDD da ya dauki matakai domin magance tabarbarewar yanayi a Syria
2018-04-12 16:27:32 cri
Jiya Laraba 11 ga wata, babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya fidda wata sanarwa, inda ya yi kira ga kwamitin sulhun MDD da ya dauki matakai domin magance tabarbarewar yanayi a kasar Syria.

Cikin sanarwar ya ce, ya buga waya ga zaunannun wakilan kasashe 5 na MDDr domin jaddada damuwarsa matuka kan yanayin da kasar Syria ke ciki a halin yanzu, inda ya kuma jaddada bukatar daukar matakan magance tabarbarewar yanayi a kasar.

Haka kuma, ya ce, labarin da aka fitar game da kaddamar da hare-haren makamai masu guba a kasar Syria ya bata masa rai kwarai da gaske, kana yana bakin ciki sakamakon kasa cimma matsaya guda kan wannan batu a kwamitin sulhu na MDDr. Ya ce, babban burinsu shi ne fitar da al'ummomin kasar Syria daga mawuyacin hali. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China