in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Turkiya, Rasha da Iran za su yi ganawa don tattauna batun Syria
2018-04-01 13:33:11 cri
A ranar 31 ga watan Maris da ya gabata, fadar shugaban kasar Turkiya ta fidda wata sanarwa inda ta bayyana cewa, shugabannin kasashe uku da suka hada da Turkiyar, Rasha da Iran za su yi ganawa a Ankara babban birnin kasar Turkiyan, a ranar 4 ga watan nan da muke ciki, domin yin tattaunawa kan batun Syria.

Cikin sanarwar, an kuma bayyana cewa, shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin za su halarci kwamitin kolin hadin gwiwar kasashen Turkiya da Rasha da za a yi a ranar 3 ga wata. Ban da haka kuma, shugabannin biyu za su halarci bikin aza harsashi na tashar nukiliya ta samar da wutar lantarki ta farko ta kasar Turkiya watau tashar Akkuyu da za a yi a wannan rana.

A ranar 22 ga watan Nuwamban shekarar 2017, shugabannin kasashen Turkiya, Rasha da Iran sun yi ganawa a birnin Sochi na kasar Rasha, inda suka yi musayar ra'ayoyi kan ci gaban yanayin da ake ciki game da batun kasar Syria da kuma hanyoyin warware matsalar da abin ya shafa da dai sauransu, sa'an nan sun fidda wata sanarwa cikin hadin gwiwa, yayin da suka yi kira da a gudanar da cikakken zaman taron neman sulhu kan kasar Syria.

Daga bisani kuma, a ranar 30 ga watan Janairu, an yi cikakken zaman taron yin shawarwari kan batun kasar Syria a birnin Sochi, inda bangarori daban daban suka fidda wata sanarwa cikin hadin gwiwa, yayin tsaida kuduri kan kafa kwamitin kundin tsarin mulkin kasar ta Syria. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China