in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yabawa MDD da ta yi kokarin sassauta halin jin kai a kasar Syria
2018-03-13 17:27:09 cri
Zaunannen wakilin Sin dake MDD Ma Zhaoxu ya bayyana a jiya Litinin cewa, Sin ta yabawa MDD da babban sakataren MDD da yadda suka yi kokarin sassauta halin jin kai a yankunan kasar Syria, kana ya jaddada cewa, ya kamata a tabbatar da aiwatar da kuduri mai lamba 2401.

Jami'in ya bayyana a gun taron kwamitin sulhun MDD kan batun jin kai na kasar Syria da aka gudanar a wannan rana cewa, Sin ta yi kokarin samar da gudummawa ga jama'ar kasar Syria. A watan da ya gabata, Sin ta kara samar da gudummawar ruwa da abinci da hidimar kiwon lafiya da wurin kwana da sauransu ga jama'ar kasar Syria da suka rasa gidajensu ta kafar kwamitin Red Cross na duniya. Kasar ta ki amincewa ga duk irin aiki na kai hari ga fararen hula, ya kamata a magance tsananta irin halin da ake ciki a kasar.

Ya kara da cewa, a ranar 24 ga watan Febrairu, bangarori daban daban na kwamitin sulhun MDD sun zartas da kuduri mai lamba 2401, ta haka an tabbatar da hadin kan kwamitin sulhun, da samar da dama ga tsagaita bude wuta da dakatar da rikice-rikice a kasar Syria.

Ma Zhaoxu ya ce, Sin ta kalubalanci bangarori daban daban da abin ya shafa da su yi kokari tare da gudanar da ayyukansu don tabbatar da aiwatar da kuduri mai lamba 2401 yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China