Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya taya wa shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi murnar sake zama shugaban kasar ta Masar a karo na biyu. Sa'an nan ya yi nuni da cewa, kasar Sin na fatan yin kokari tare da Masar, wajen daga matsayin huldar abokantaka da ke tsakanin kasashen 2 daga dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare zuwa wani sabon mataki. (Tasallah Yuan)