in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi tir da harin ta'addanci a Masar
2017-07-10 20:41:13 cri

Ranar 7 ga wata ne, wasu masu tsattsauran ra'ayi suka kai hari a wajen binciken ababan hawa na sojoji dake garin Rafah a arewacin Sinai a kasar Masar, inda mutane gomai suka rasa rayukansu ko suka jikkata.

Dangane da lamarin, Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana yau Litinin a nan Beijing cewa, kasar Sin ta yi tir da wannan harin ta'addanci, kana tana adawa da duk wani nau'i na ta'addanci, tana kuma goyon bayan kokarin kasar Masar na yaki da 'yan ta'adda, da tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a kasar. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China