in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Syria ta ce 'yan tawaye na shirin amfani da makamai masu guba wajen kai hari yankin Ghouta
2018-03-02 12:33:32 cri
Kamfanin dillancin labarai na Syria wato SANA, ta ruwaito Rundunar sojin kasar na cewa, ta samu wani sahihin rahoto dake cewa 'yan tawayen dake gabashin yankin Ghouta na shirin amfani da makamai masu guba don yi wa dakarun Gwamnatin kasar sharri.

Cikin wata gajeriyar sanarwar da rundunar sojin ta fitar, ta ce 'yan tawayen dake gabashin Ghouta, sun samu umarnin yin amfani da makamai masu guba a yankin domin yi wa sojojin gwamnati sharri.

Rahotanni na cewa, 'yan tawayen za su yi amfani da sinadarai masu guba a kusa da iyakarsu da sojojin Gwamnati, inda za su kai hari kan fararen hula, ta yadda kasashen Birtaniya da Amurka da sauran kasashen Turai za su zargi dakarun Syria da kai harin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China