Haka kuma, a yayin da yake tsokaci kan shirin "Ziri daya da Hanya daya", ya bayyana cewa, tabbas ne shirin zai karfafa mu'amalar dake tsakanin kasa da kasa, da kuma kawo sauki ga ciniki dake tsakanin kasa da kasa, ba wanda zai ki shiga cikin shirin, kuma a ko da yaushe kasarsa ta Zimbabwe zai nuna goyon baya ne kan shirin.
Game da taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka da za a yi a watan Satumba na shekarar bana kuwa, shugaba Mnangagwa ya bayyana cewa, ya riga ya sami takardar gayyata, kuma zai halarci dandalin da za a yi a birnin Beijing. (Maryam)