in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar adawa mai goyon bayan Mugabe ta nada shugaban da zai kalubalanci shugaban kasar mai ci a zaben da za a yi
2018-03-06 09:54:37 cri
An kafa wata sabuwar Jam'iyya da aka yi ammana ta na goyon bayan tsohon shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe, domin kalubalantar Shugaban kasar kuma shugaban Jam'iyyar ZANU PF mai mulkin kasar a zaben da aka shirya yi a tsakiyar shekarar nan.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya, sabuwar Jam'iyyar ta New Patriotic Front wato NPF, ta sanar da nada Ambrose Mutinhiri a matsayin shugaban Jam'iyyar kuma 'dan takarar shugaban kasa a zaben.

Ambrose Mutinhiri wanda tsohon Brigedier Janar ne kuma dan gwagwarmayar neman 'yancin kasar, ya yi murabus daga Jam'iyyar ZANU PF da majalisar dokokin kasar ne a ranar Juma'ar da ta gabata, domin nuna adawarsa da abun da ya kira 'sabawa kundin tsarin mulki wajen cire Shugaba Mugabe'.

Shugaban na sabuwar Jam'iyyar NPF, ya taba rike mukamin minista a gwamnatin tsohon shugaba Mugabe.

Robert Mugabe dai ya yi murabus ne a watan Nuwamban bara, bayan ya fuskanci matsin lamba daga sojoji, inda aka maye gurbinsa da Emmerson Mnangagwa da ya sauke daga mukamin mataimakin shugaban kasa makonni biyu kafin ya yi murabus, sanadiyyar rikicin da ake a jam'iyyar game da wanda zai maye gurbin shugaban kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China