in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar shugaban kasar Zimbabwe za ta sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe
2018-03-30 20:18:24 cri
A ranar 2 ga watan Afrilu, shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa zai kawo ziyara nan kasar Sin. Game da hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau 30 ga wata cewa, ziyarar shugaba Mnangagwa, za ta kara sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe.

A gun taron manema labaru da aka gudanar a wannan rana, Lu Kang ya bayyana cewa, Sin ta dora muhimmanci sosai kan dangantakar dake tsakaninta da kasar Zimbabwe, tana kuma fatan kokari tare da kasar Zimbabwe, wajen inganta dangantakar dake tsakaninsu don amfanin kasashen biyu da jama'arsu.

An gama aikin fadada tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa dake kudancin gabar Kariba, wadda kasar Sin ta tattara kudin aiwatarwa a kasar ta Zimbabwe. Lu Kang ya bayyana cewa, bayan kammala aikin, za a fadada samar da wutar lantarki, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'ummar Zimbabwe, kuma Sin na farin ciki matuka game da hakan.

Ya ce akwai irin wadannan ayyuka da dama na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, wanda hakan ke shaida cewa, hadin gwiwa da zuba jari da kasar Sin ta yi a kasashen Afirka, sun taimakawa kasashen nahiyar wajen samar da kayayyaki, da samun moriyar tattalin arziki da zamantakewar al'umma, wadanda kuma gwamnatocin kasashen Afirka da jama'arsu ke maraba da su. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China