in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta tsai da kudurin tsawaita wa'adin aikin tawagar bada taimako a Somaliya
2018-03-28 12:14:50 cri
Jiya Talata, kwamitin sulhu na MDD ya zartas da kuduri mai lambar 2408, inda aka tsai da kudurin tsawaita wa'adin aikin tawagar bada taimako dake Somaliya zuwa ranar 31 ga watan Maris na shekarar 2019.

Haka kuma, an nuna yabo ga tawagar domin babbar gudummawa da ta bayar kan goyon bayan kasar Somaliya wajen neman sulhu da shimfida zaman lafiya, da warware sabani da kuma ba da taimako a yayin babban zaben kasar. A sa'i daya kuma, kwamitin ya sake jaddada girmamawarsa kan 'yancin kan kasar Somaliya da kuma cikakken zaman kasar, ya kuma bayyana muhimmiyar ma'ana ta hana yaduwar rikice-rikicen a yankunan kasar ta Somaliya.

An kafa tawagar bada taimako ga kasar Somaliya ne a watan Yuni na shekarar 2013, bisa kudurin kwamitin sulhu na MDD mai lambar 2102. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China