in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Somaliya sun bindige wasu dakarun kungiyar al-Shabaab 7
2018-01-30 10:14:04 cri
Gwamnatin kasar Somaliya ta tabbatar a jiya Litinin cewa, sojojin gwamnatin kasar sun gwabza wani kazamin fada da dakarun kungiyar al-Shabaab a jihar Bay dake kudancin kasar, lamarin da ya kai ga kashe mayakan kungiyar a kalla 7, tare da raunata wasu, yayin da sojojin gwamnati kuma 4 suka rasa rayuka, ciki har da wani babban hafsa.

Kungiyar al-Shabaab wata kungiya ce ta masu tsattsauran ra'ayi, wadda ke da alaka da kungiyar al-Qaeda. A shekarun nan, dakarun al-Shabaab sun yi ta kaddamar da hare-haren ta'addanci a kasar Somaliya da makwabtanta.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China