in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya halarci taron tattanawa da wakilan jama'ar birnin Chongqing
2018-03-11 14:02:38 cri

Jiya Asabar, a yayin da tawagar wakilan jama'ar birnin Chongqing ta halarci taron tattaunawa kan rahoton gwamnati, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada cewa, aikin gina yanayin siyasa mai adalci da tsari wanda babu cin hanci da karbar rashawa shi ne muhimmiyar bukatar da ake da shi na kiyaye ikon mulkin kasa na Jam'iyyar Kwaminis ta Sin wato JKS, kana, muhimmin abu ne wajen inganta bunkasuwar ayyukan JKS da kuma kyautata yanayin siyasar JKS, ta yadda za a iya bada tabbaci wajen cimma burin yin kwaskwarima a kasar Sin da kuma neman ci gaba.

Bugu da kari, ya ce, ya kamata a mai da hankali kan ayyuka na wasu muhimman shugabannin kasar, domin su zama abin koyi da kuma yin jagoranci ga al'ummomin kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China