in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a kara raya tattalin aiziki mai bude kofa ga waje, in ji Xi Jinping
2018-03-08 09:35:53 cri

Jiya Laraba, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya nuna sabbin bukatu ga lardin Guangdong game da neman ci gaba a sabon zamani, a yayin da tawagar wakilan jama'ar lardin Guangdong ta halarci taron yin nazari kan rahoton gwamnati. Shugaba Xi ya ce, ya kamata lardin Guangdong ya daga burinsa na neman bunkasuwa, ya dauki matakai masu karfi wajen inganta aikin bude kofa ga waje bisa dukkan fannoni, da kuma gaggauta neman bunkasuwar tattalin arziki mai bude kofa ga waje. Sa'an nan kuma, ya kamata lardin Guangdong ya dukufa wajen tsara sabon tsarin raya harkokin ciniki da kuma shiga cikin ayyukan aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya cikin himma da kwazo.

Bugu da kari, shugaba Xi ya ce, ya kamata lardin Guangdong ya kama muhimmiyar dama ta raya yankunan Guangdong, Hong Kong da Macau, da kuma yin hadin gwiwa da bangarorin Hong Kong da Macau wajen ciyar da ayyukan da abin ya shafa gaba, ta yadda za a kafa wani yanki na birane masu ci gaba a duniya.

A yayin taron, shugaba Xi ya saurari jawabin da wakilan lardin Guangdong suka gabatar, inda ya kuma yi shawarwari tare da su. Wannan shi ne karo na biyu da Xi Jinping ya halarci taron wakilan na lardin Gongdong, bayan na shekarar 2014, wanda shi ne karo na farko da ya halarci taron na wakilan lardin Guangdong.

Shekarar bana shekara ce ta cikon shekaru 40 da kasar Sin ta fara bude kofa ga waje, kana, lardin Guangdong ya zama lardin dake kan gaba wajen aiwatar da harkokin bude kofa ga waje, shi ya sa, jawabin da shugaba Xi ya gabatar wa tawagar wakilan lardin Guangdong ya janyo hankulan bangarori daban daban kwarai da gaske. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China