in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a rage kudin haraji domin ci gaba da samar da sauki ga kamfanonin kasar Sin
2018-03-07 11:11:52 cri
Ministan harkokin kudin kasar Sin Xiao Jie, ya bayyana a yau Laraba cewa, a bana, kasar Sin za ta ci gaba da rage kudin haraji domin samar da sauki ga kamfanonin dake kasar da kuma sa musu kaimi wajen neman ci gaba.

Haka kuma ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da yin kwaskwarima kan tsarin karbar kudin haraji domin taimakawa bunkasar sana'o'i daban daban a kasar. A sa'i daya kuma, za a yi kwaskwarima kan tsarin haraji kan kudin shiga da mutanen kasar ke samu, tare da karfafa taimakon da za a ba kanana, da matsakaitan kamfanonin kasar.

Bugu da kari, ya ce, bisa kididdigar da aka yi, gaba daya, za a rage haraji na kudin yuan biliyan dari 8 cikin shekarar 2018, bayan fara aiwatar da manufofin rage haraji a kasar.

Har ila yau, za a dadaita tsarin asusun gwamnatocin kasar da kuma tsarin karbar kudi kan harkokin gudanarwa da ba da hidima da dai sauransu, inda gaba daya za a rage kudin yuan biliyan dari 3 a wadannan fannoni. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China