in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta cimma burin karuwar kashi 6.5 bisa 100 na tattalin arziki a bana
2018-03-06 13:41:04 cri
Shugaban hukumar raya kasa da yin kwaskwarima ta kasar Sin He Lifeng ya bayyana a yau Talata cewa, akwai tabbacin cewa, kasar Sin za ta cimma burin samun karuwar kashi 6.5 bisa dari na tattalin arzikinta a cikin shekarar bana.

Yana ganin cewa, a bana, za a ci gaba da samun karuwar kashe kudi a duk fadin kasar Sin, sabo da bunkasuwar sabbin sana'o'i da sana'o'in ba da hidima na zamani, lamarin da zai ba da babbar gudummawa ta kashi 60 bisa dari ga ci gaban tattalin arzikin kasar.

Haka kuma, ya ce, a halin yanzu, ana dukufa wajen tsara wasu manufofin da za su habaka harkokin zuba jari a fannoni daban daban a kasar, wadanda za su ba da gudummawar kashi daya bisa uku ga ci gaban tattalin arzikin kasar.

A sa'i daya kuma, za a ci gaba da samun karuwa a fannin shiga da fitar da hajoji a tsakanin Sin da kasashen ketare, wanda shi ma zai ba da gudummawa ta kashi 8 zuwa 9 bisa dari ga bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China