in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a kafa tsarin hakkin dan Adam mai adalci da kuma mai nuna fahimtar juna
2018-03-01 10:51:51 cri
Jiya Laraba, zaunannen wakilin kasar Sin dake ofishin MDD a birnin Geneva, kana wakilin kungiyoyin kasa da kasa dake kasar Switzerland Yu Jianhua, ya gabatar da jawabi a yayin taron kwamitin hakkin dan Adam na MDD karo na 37 inda ya nuna cewa, ya kamata gamayyar kasa da kasa su yi hadin gwiwa wajen gina dunkulewar mutanen kasa da kasa, da kuma inganta ayyukan gina tsarin hakkin dan Adam mai adalci da kuma mai nuna fahimtar juna.

A cikin jawabinsa, Yu Jianhua ya gabatar da manufofi guda hudu da suka hada da: na farko, a nemi ci gaban kasa da kasa ta yadda za a bada gudummawa kan aikin kare hakkin dan Adam, domin ci gaba shi ne mabudi na warware dukkan matsalolin da abin ya shafa. Shi ya sa, ya kamata a aiwatar da jadawalin neman dauwamammen cigaba nan da shekarar 2030 da MDD ta tsara, domin kawar da talauci mai tsanani a duk fadin duniya.

Na biyu shi ne, ya kamata a kare tsaron kasa da kasa domin inganta harkokin kare hakkin dan Adam, domin yake-yake da tashe-tashen hankula su kan haddasa keta hakkin dan Adam.

Na uku kuma, ya kamata a ciyar da aikin kare hakkin dan Adam gaba ta hanyar yin hadin gwiwa.

A karshe ya ce, ya kamata a karfafa yanayin adalci wajen ciyar da aikin gaba. A halin yanzu, yawan mutanen kasashe masu tasowa ya kai kashi 80 bisa dari a duk fadin duniya, ya dace a kyautata matsayinsu kan wannan al'amari wajen nuna bukatunsu da kuma shawarwarinsu.

Bisa labarin da aka samu, an ce, an bude taron kwamitin hakkin dan Adam na MDD karo na 37 a birnin Geneva a ranar 26 ga watan Fabrairu, kuma za a kawo karshen taron a ranar 23 ga watan Maris. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China