in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi muhawara a taron kwamitin kare hakkin bil Adam na MDD
2017-09-28 11:03:47 cri
A jiya Laraba ne, aka yi muhawara a taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD karo na 36 a birnin Geneva na kasar Switzerland, inda wakilai suka nuna damuwa kan rashin yin hakuri da juna, musamman ma a fannonin wariyar launin fata da nuna kabilanci da kuma nuna kiyayya ga baki.

Kuma babban taken muhawarar shi ne yadda aka aiwatar da sanarwar Durban da kuma ka'idojin gudanarwa, watau DDPA.

A yayin taron, wakilin kasar Sin ya bayyana cewa, sanarwar DDPA tana da muhimmiyar ma'ana ga kasashen duniya wajen yaki da wariyar launin fata da sauran abubuwa masu nasaba da gajen hakuri. A halin yanzu, ana ci gaba da fuskantar mummunar nuna wariyar launin fata a wasu kasashen duniya, lamarin da ya haddasa kiyayya a tsakanin kabilu daban daban, da kuma tabarbarewar yanayin zaman rayuwar 'yan gudun hijira, inda a wasu lokutan aka kai wa wasu kanannan kabilu hare-hare da ba su kamata ba.

Bugu da kari, wakilai masu halartar muhawarar sun yi kira da a aiwatar da sanarwar DDPA yadda ya kamata, domin za ta taimaka wajen warware kalubalolin dake shafar wariyar launin fata da kuma nuna kiyayya ga baki dai sauran aikace-aikace masu nasaba da rashin hakuri da juna. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China