in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin hakkin dan Adam na MDD ya zartas da kudurin inganta harkokin kare hakkin dan Adam ta hanyar neman ci gaba
2017-06-24 13:58:05 cri
A ranar 22 ga wata ne Kwamitin kare hakkin dan Adama na MDD ya zartas da kudurin babbar gudummawa da ci gaban duniya zai samar wa aikin kare hakkin dan Adam da kasar Sin ta fidda.

Wannan kuma shi ne karo na farko, da kwamitin kare hakkin dan Adama na MDD ya zartas da wani kudurin da ya shafi harkokin neman ci gaba.

Rahotanni sun bayyana cewa, kudurin ya samu amincewar kasashe sama da 70.

Zaunannen wakilin kasar Sin dake ofishin Geneva na MDD Ma Zhaoxu ya bayyana cewa, wannan kuduri shi ne babbar gudummawa da kasar Sin ta samar wa kasa da kasa wajen gudanar da ayyukan kare hakkin dan Adam, kuma tabbas, zai kyautata matsayin kasashe masu tasowa kan wannan harka, yayin ciyar da ayyukan kare hakkin dan Adam na kasa da kasa gaba, cikin himma da kwazo. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China