Haka kuma, ya ce, karancin kudaden Falesdinu ya haddasa raguwar tattalin arzikinta, yayin da ake karfafa dogaro kan Isara'ila. Ya ce, ya kamata a yi amfani da sauran kudade da ake iya samu ta wasu sassa a yankunan Falesdinu amma ban da na Isra'ila.
Sa'an nan, ya jaddada cewa, ya kamata a dauki matakai da dama domin cimma wannan buri, musamman ma a fannin karfafa kwarewar al'ummomin kasar wajen samar da kayayyaki ta fuskar ayyukan noma, da masana'antu. A sa'i daya kuma, a dakatar da shigar da hajojin Isra'ila a yankunan Falasdinawa. (Maryam)