in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Falesdinu ya yi allah wadai da matakin da Isra'ila ta dauka kan Masallacin Al-Aqsa
2017-07-15 13:47:54 cri
Shugaban Falesdinu Mahmoud Abbas ya gana da firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ta wayar tarho, inda ya yi Allah wadai tare da sukar matakin rufe Masallacin Al-Aqsa da kasar Isra'ila ta yi, inda ya kuma bukaci Isra'ila ta dakatar da dukkan aikace-aikacen da suka shafi rufe Masallacin, yana mai gargadin kada a keta matsayin tarihi da na addini na Masallacin Al-Aqsa.

Rahotanni sun bayyana cewa, yayin ganawar tasu a jiya Jumma'a, Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya jaddada cewa, ba za a sauya yanayin da Masallacin ke ciki ba, har sai bangarorin da ke adawa da juna sun dauki matakan da za su dace na tsayar da rikice-rikicen dake tsakaninsu.

Da safiyar jiya Juma'a ne, wasu mutane uku suka budewa 'yan sandan Isra'ila wuta a tsohon birnin Jerusalem, harin da ya haddasa mutuwar 'yan sanda biyu, daga bisani kuma, 'yan sanda sun harbe maharan 3.

Bayan aukuwar harin ne kuma, Isra'ila ta rufe Masallacin Al-Aqsa dake wurin, al'amarin da ya hana Musulmai yin salla a masallacin. Baya ga wannan, Isra'ila ta kuma kulle kofar fita ta birnin dake yammacin kogin Jordan. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China