in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe taron kolin kungiyar AU karo na 30
2018-01-30 09:24:25 cri

Jiya Litinin ne, aka rufe taron kolin kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU karo na 30 a birnin Addis Ababa na kasar Habasha.

A yayin taron, mambobin kungiyar AU sun tattauna game da matsalar cin hanci da rashawa, inda suka tsara wasu matakan warware wannan matsala. Haka kuma kasashen kungiyar sun sanar da kafa kasuwar sufurin jiragen sama a tsakanin kasashen Afirka a hukunce, da jaddada muhimmancin hadin gwiwar mambobin kungiyar wajen yaki da ta'addanci.

A jawabinsa yayin rufe taron, sabon shugaban kungiyar, kana shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame ya bayyana cewa, an tsai da wasu muhimman kudurori a yayin taron kolin kungiyar AU na wannan karo, wadanda za su taimaka ga bunkasuwar kasashen Afirka a nan gaba. Haka kuma, ya ce, ya kamata kasashen Afirka su hada kai don karfafa dunkulewar kasashen Afirka waje guda.

A nasa jawabin, shugaban hukumar zartaswar kungiyar ta AU Moussa Faki ya bayyana cewa, yaki da cin hanci da karbar rashawa shi ne babban nauyin dake wuyan kasashen Afirka, lamarin da ke damun al'ummomin kasashen kwarai da gaske. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China