in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron shugabannin kungiyar AU karo na 30 a Habasha
2018-01-29 10:55:36 cri

Jiya Lahadi, aka bude taron shugabannin kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU karo na 30 a hadkwatar kungiyar dake birnin Addis Ababa na kasar Habasha.

Babban taken taro na wannan karo shi ne, "Cimma nasarar yaki da cin hanci da rashawa, hanya mafi dacewa ta farfadowa da kasashen Afirka". A kwanaki biyu na taron, shugabanni mambobin kungiyar za su tattauna batutuwan yiwa kungiyar gyaran fuska,da batun dunkulewar kasashen Afirka da kuma yaki da cin hanci da karbar rashawa da dai sauransu.

A jawabinsa yayin bikin bude taron, shugaban hukumar zartarwar kungiyar AU Moussa Faki ya bayyana cewa, ya kamata a gaggauta yiwa kungiyar AU kwaskwarima, domin kara karfin kungiyar na inganta dunkulewar kasashen nahiyar, hanya mafi dacewa don neman bunkasuwar kasashen Afirka baki daya.

Haka kuma, ya ce, a halin yanzu, an sami babban ci gaba a matakin farko na shawarwarin kafa yankin ciniki cikin 'yanci a nahiyar Afirka, kuma ana sa ran zartas da yarjejeniyar yankin ciniki cikin 'yanci a taron kolin kungiyar AU na wannan karo. A sa'i daya kuma, a yayin taron ne, ake fatan bude kasuwar sufurin jiragen sama a tsakanin kasashen Afirka. Haka kuma ya ce, ya kamata mambobin kungiyar su mai da hankali kan batun yaki da cin hanci da karbar rashawa, domin hana fitar da kudaden da aka sata ba bisa doka ba daga nahiyar Afirka zuwa ketare. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China