in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar LAS tana son karfafa hadin gwiwarta da kungiyar AU kan ayyukan kiyaye zaman lafiya da tsaro
2018-01-29 10:56:41 cri
Jiya Lahadi, babban sakataren kungiyar tarayyar kasashen Larabawa ta (LAS) Ahmad Abdoul Gheit ya bayyana a yayin taron shugabannin kungiyar AU karo na 30 a birnin Addis Ababa na kasar Habasha cewa, kungiyar tana son karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU kan harkokin kiyaye zaman lafiya da tsaro.

Mr. Gheit ya kara da cewa, kungiyar LAS tana mai da hankali sosai kan dangantakar abokantaka dake tsakaninta da kungiyar AU, kuma a nan gaba, za ta dukufa wajen karfafa hadin gwiwar bangarorin biyu a fannin ayyukan kiyaye zaman lafiya.

Bugu da kari, ya ce, a halin yanzu, kasashen Larabawa da kasashen Afirka suna fuskantar matsalolin tashe-tashen hankula, a don haka ya kamata su dukufa tare da yin hadin gwiwa domin warware wadannan matsalolin yadda ya kamata.

Ya kuma jaddada cewa, kungiyar LAS da kungiyar AU za su karfafa mu'amalar dake tsakaninsu, sa kuma hadin gwiwa domin yaki da ta'addanci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China