in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zimbabwe ya bukaci a karfafa dangantaka tsakanin mambobin AU
2018-01-28 12:55:59 cri
Sabon shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, ya halarci taron kolin kungiyar tarayyar Afirka (AU) a karon farko tun bayan da ya dare shugabancin kasar, inda ya jaddada cikakken goyon bayan kasar Zimbabwe game da harkokin da suka shafi kungiyar ta AU.

Mnangagwa, ya bayyana tsohon shugaban kasar ta Zimbabwe Robert Mugabe, a matsayin dan kishin Afrika na hakika, kana ya bukaci mambobin kasashen na AU da su kara karfafa dangantar zamantakewa da tattalin arziki a tsakaninsu.

Mnangagwa, yayi wannan tsakaci ne a lokacin da ya halarci taron sabon shirin raya cigaban Afrika (NEPAD), wanda aka gudanar a gefen taron kolin na AU karo na 30, wanda ke gudana a Addis Ababa babban birnin kasar Habasha.

Yace kasar Zimbabwe tana matukar alfahari da kasancewarta daya daga cikin wannan babbar kungiya wanda ta kasance tamkar iyali ne guda, ya kara da cewa, kasarsa a shirye take ta marawa dukkan ayyukan kungiyar ta AU baya don cigaban nahiyar Afrika.

Mnangagwa ya bayyana aniyar gwamnatinsa na yin aiki tare da dukkannin kasashen Afrika, a bisa tsarin daidaiku da kuma tsarin gamayyar kasashen.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China