in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci da a samar da managartan dokoki na bunkasa sashen hakar ma'adanai a Afirka
2018-01-26 09:28:53 cri
Kwamishinan kungiyar AU mai lura da harkokin cinikayya da raya masana'antu Muchanga Albert, ya yi kira ga kasashen nahiyar Afirka, da su samar da managartan ka'idoji na cin gajiya daga sashen hakar ma'adanai a nahiyar.

Muchanga Albert ya yi kiran ne yayin wani taron zantawa da manema labarai, a gefen taron shugabannin kungiyar karo na 30 da yanzu haka ke gudana a birnin Addis Ababa na kasar Habasha. Ya ce nahiyar na bukatar dokoki da tsare tsare, wadanda za su share fagen cin gajiya daga fannin hakar ma'adanai yadda ya kamata.

Kungiyar AU ta sha bayyana nahiyar Afirka a matsayin wadda ke sahun gaba wajen fidda ma'adanai da tarin albarkarun kasa, amma kuma har yanzu tana fuskantar karancin tsarin binciken yanayin karkashin kasa, wanda hakan ke tauye gajiyar da nahiyar ke iya samu daga albarkatun na ta.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China