in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan ziyarar da Theresa Mary May za ta kawo kasar Sin za ta zurfafa huldar da ke tsakanin Sin da Birtaniya
2018-01-25 19:56:14 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta sanar da cewa, Theresa Mary May, firaministar kasar Birtaniya za ta kawo ziyarar aiki kasar Sin daga ranar 31 ga watan Janairu zuwa ranar 2 ga watan Fabrairu, bisa gayyatar da takwaranta na kasar Sin Li Keqiang ya yi mata, inda za ta halarci taron shekara-shekara na firaministocin kasashen 2.

Madam Hua wadda ta fadi haka a yau Alhamis a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing. Ta kuma ce, ziyarar da Theresa Mary May za ta kawo kasar Sin, ita ce ta farko tun bayan da ta zama firaministar Birtaniya, ziyarar da take da muhimmiyar ma'ana wajen raya huldar da ke tsakanin Sin da Birtaniya a sabon halin da ake ciki. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China