in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana maraba da ziyarar da firaministar kasar Birtaniya za ta kawo
2017-02-08 20:02:28 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar yau a nan birnin Beijing cewa, shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 45 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Sin da Birtaniya, wannan wata sabuwar dama ce ta raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Sin tana maraba da ziyarar da firaministar kasar Birtaniya Theresa May za ta kawo nan kasar, kuma ta zo a lokacin da ya dace.

Rahotanni na cewa, kakakin ofishin firaministar kasar Birtaniya ya bayyana a kwanakin baya cewa, firaminista Theresa May za ta kawo ziyara kasar Sin a bana. Game da wannan batu, Lu Kang ya bayyana cewa, a watan Satumban bara ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da Theresa May a lokacin da ta halarci taron kolin kungiyar G20 da aka gudanar a birnin Hanzhou na kasar Sin, inda shugabannin biyu suka tabbatar da makomar bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 45 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu, Sin tana son hada kai tare da kasar Birtaniya domin kara raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a karni na 21 yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China