Yau Talata ne Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya sanar da cewa, kasashen Sin da Birtaniya sun yanke shawarar gudanar da taron tattaunawa a tsakaninsu ta fuskar tattalin arziki da harkokin kudi karo na 9 a nan Beijing daga ranar 15 zuwa 16 ga wata, inda mataimakin firaministan kasar Sin Ma Kai da sakataren kudi na Birtaniya Philip Hammond za su shugabanci taron tattaunawar tare. (Tasallah Yuan)