in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Syria ta yi Allah wadai da matakan soja da Turkiya ta dauka a yankin Afrin mallakarta
2018-01-21 13:23:43 cri
Jiya Asabar, ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria ta fidda wata sanarwa, inda ta yi Allah wadai da matakan soja da kasar Turkiya ta dauka a birnin Afrin mallakin kasar Syriar, haka kuma ta musanta ikirarin da tace kasar Turkiya ta yi kan wannan al'amari na cewar wai dama Turkiya ta taba sanar wa bangaren Syria kafin ta fara aiwatar da matakan soja a birnin.

Cikin sanarwar da ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria ta fidda, ta kuma bayyana cewa birnin Afrin shine wani yankin dake karkashin ikon kasar Syria, matakan soja da kasar Turkiya ta dauka a wannan birnin sun keta ikon kasar Syria da kuma 'yancin kanta. Shi yasa, kasar Syria ta yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su yi Allah wadai kan matakan da kasar Turkiyar ta dauka, su kuma dauki matakai yadda ya kamata domin tsayar da matakan soja da kasar Turkiya take aiwatarwa a birnin Afrin mallakinta.

A ranar 20 ga wata, shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan, ya sanar da cewa, sojojin kasarsa zasu fara aiwatar da matakan soja a birnin Afrin dake arewacin kasar Syria.

Sa'an nan, a wannan rana da yamma, hedkwatar bada nasiha ga rundunonin sojojin kasar Turkiya ta bada sanarwa cewa, matakan sojan da kasarta ta dauka sun kasance "matakai ne na kare kanta bisa doka", kuma, kasar Turkiya tana mutunta ikon mulki da kuma 'yancin kan kasar ta Syria. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China