in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za'a gudanar da taron Geneva game da rikicin Syria a watan Janairu
2017-12-22 09:36:07 cri
Wakilin musamman na MDD a kasar Syria Staffan de Mistura, ya bayyana cewa an shirya gudanar da taron tattaunawar Geneva karo na 9 game da warware rikicin Syria a tsakiyar watan Janairun badi.

De Mistura ya bayyana hakan ne a lokacin taron manema labarai jim kadan bayan kammala tattaunawa da ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavrov dana tsaro Sergei Shoigu.

Ya ce sabon zagayen tattaunawar ta Geneva zata mayar da hankali ne game da yadda za'a samu cikakken tsarin aiwatar da kudurin kwamitin tsaron MDD mai lamba 2254 wanda aka amince da shi a watan Disambar 2015, wanda ya ayyana bukatar tsara kundin tsarin mulkin kasar da kuma shirya zabe a Syriar.

Wakilin na MDD ya ce, yana sa ran za'a samu taimako daga dukkan bangarorin da abin ya shafa, ciki har da kasar Rasha, domin tabbatar da ganin taron tattaunawar dake tafe ya samu gagarumar nasara sama da wadanda aka shirya a baya, musamman ma wanda aka kammala a farkon wannan watan ba tare da cimma nasara ta azo a gani ba.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China