Ministan harkokin kiwon lafiya na kasar Zambia Chitalu Chilufya ya bayyana a wani taron manema labaru jiya Talata cewa, ya zuwa yanzu, mutane 2802 ne suka kamu da cutar kwalara a kasar, yayin da mutane 64 suka rasa rayukansu sakamakon kamuwa da wannan cuta. Yanzu haka dai masu fama da cutar 218 na samun jinya a kasar.
Ministan ya kara da cewa, daga ranar 10 ga wata, ma'aikatar ta fara yi wa mutane miliyan 2 allurar rigakafin cutar a wasu wuraren da aka fi fama da cutar dake birnin Lusaka. Ya ce za a shafe kwanaki 7 zuwa 10 ana gudanar da aikin. (Tasallah Yuan)