in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zambiya za ta kammala zamanantar da shirin ba da lasisin ma'adanai a shekara mai zuwa
2016-12-17 12:30:48 cri
Gwamnatin kasar Zambiya ta kuduri aniyar kammala shirin samar da lasisi ta hanyar amfani da na'ura mai kwakwalwa a fannin hakar ma'adanai a shekara mai zuwa.

Ministan ma'adanai na kasar Christopher Yaluma, shi ne ya tabbatar da hakan, ya ce gwamnatin kasar za ta kammala aikin mayar da tsarin samar da lasisin a fannin ma'adanai ta hanyar na'urar kwamfuta da kuma shafukan intanet domin ya dace da zamani, kana domin aikin ya dinga gudana cikin sauri.

Ya ce idan shirin ya tabbata, zai kara janyo hankulan masu zuba jari a fannin hakar ma'adinan kasar, kuma zai bada damar gudanar da aikin samar da lasisin ba tare da rufa rufa ba.

Cikin wani jawabi da ministan ya gabatar a gaban majalisar dokokin kasar ya ce "za'a samu karuwar masu zuba jari a fannin ma'adanan, kuma gwamnati za ta samu karin kudaden shiga ta hanyar kudaden da masu yin rajistar neman lasisin za su biya." (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China