Gwamnatin kasar Zambiya ta bayyana cewa, za ta karfafa huldar diplomasiyya da tattalin arziki a tsakaninta da Amurka, ta yadda kasar da ke kudanacin Afrika za ta amfana daga gwamnatin Donald Trump.
Ofishin jakadancin Zambiya dake Amurka ya bayyana cewa, kasar Zambiyar ta samu moriya mai yawa daga gwamnatin Amurka wadda ya baiwa kasar ta Zambiya damar karfafa dangantaka da Amurka a karkashin shirye-shiryen ilmi da kiwon lafiya.(Tasallah)