Wani babban jami'in gwamnatin kasar Zambiya yace, gwamnati tana shirin fito da wani sabon shiri wanda zai warware kalubalolin da saurin bunkasuwar biranen kasar zai iya haifarwa
Ministan kananan hukumomin kasar Vincent Mwale ya bayyana cewa, gwamnatin kasar ta fara gyaran fuska ga wasu dokoki domin shawo kan kalubalolin da cigaba biranen kasar za su iya haifarwa.
Da yake jawabi a wajen taron wuni biyu game da tsara shirin cigaban birane, ministan ya ce matakan da ake shirin dauka, za su tabbatar da cigaban kasar da kuma kyautata yanayin zaman rayuwar al'ummar kasar. (Ahmad Fagam)